Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Janye Sunan Maryam Shetty Daga Sunayen Ministoci


Dr. Maryam Shetty (Hoto: Facebook/Maryam Shetty)
Dr. Maryam Shetty (Hoto: Facebook/Maryam Shetty)

A ranar Laraba, Tinubu ya aike da jerin sunaye 19 a karo na biyu, ciki har da sunan Shetty.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya cire sunan Dr. Maryam Shetty daga jerin sunayen mutanen da ya zaba a matsayin minitoci.

Wata wasika da shugaban ya turawa Majalisar Dattawa, ta nuna cewa an cire sunan Dr. Maryam Shetty daga Kano an kuma maye gurbinta da Dr. Mariya Mairiga Mahmud.

A ranar Laraba, Tinubu ya aike da jerin sunaye 19 a karo na biyu, ciki har da sunan Shetty.

A baya ya tura sunaye 28 ga majalisar.

Kazalika Tinubu ya kara sunan tsohon karamin ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Festus Keyamo, a sauyin da ya yi wa jerin sunayen da ya aika a karo na biyu.

Shugaban Majalisar Dattawan Godswill Akpabio ne ya karanto wadannan sauye-sauye a zauren majalisar a ranar Juma’a, yayin da ake ci gaba da tantance mutanen da aka zaba.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG