Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohon Shugaban Afirka ta Kudu Zai Gurfana Gaban Kotu Bisa Zargin Cin Hanci


Tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Jacob Zuma
Tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Jacob Zuma

Ranar 6 ga watan gobe tsohon shugaban Afirka ta Kudu Jacob Zuma zai bayyana gaban kotu akan laifuka 16 da suka hada da cin hanci

A Afirka ta Kudu, kotu ta yi sammacin tsohon shugaban kasar Jacob Zuma, ya bayyana gaban kuliya ranar 6 ga watan Afrilu dangane da zargin cin hanci da rashawa.

'Yan sandan kasar suka ce jiya Litinin aka baiwa tsohon shugaban kasar sammacin, mutuminda aka tilastawa yin murabus cikin watan jiya, bayan da jam'iyyar ANC ta juya masa baya.

Hukumar da take gabatar da kararraki gaban kotu ta kasar ta fada a farkon wannan wata cewa, zata nemi gurfanar da Mr. Zuma gaban kotu kan tuhume-tuhume daban daban har 16 da suka hada da cin hanci, tafiyar da harkokin kasuwanci ta hanyoyin dasuka sabawa doka, da kuma halata kudaden haram

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG