Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsuguno Bai Kare Ba Game Da Kakakin Majalisar Dokokin Nijer Hama Amadou


Kakakin Majalisar Dokokin kasar Nijer Hama Amadou.
Kakakin Majalisar Dokokin kasar Nijer Hama Amadou.

Wata kotu ta gabatar da sammacin kama Hama Amadou.

Rikicin siyasa na ci gaba da kunno kai jiddin wala hairan a kasar jamahuriyar Nijer tun bayan zargin da aka yiwa kakakin majalisar dokoki Hama Amadou da iyalin shi cewa su na da hannu dumu-dumu a abun fallasar sayen jarirai daga kasar Najeriya.

Duk da cewa Hama Amadou ya bar kasar Nijer ya samu mafaka a kasar Faransa wata kotu ta gabatar da sammacin kamo shi, al'amarin da ya haifar da rudami, da jefe-jefen juna da kalamai marasa dadi tsakanin bangaren masu mulki da na magoya bayan Hama Amadou.

Wakilin Sashen Hausa a Niamey babban birnin kasar jamahuriyar Nijer Abdoulaye Mamane Amadou ya aiko rahoto akan wannan sabuwar badakala:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:12 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hama Amadou ya bar kasar Nijer ne a lokacin da aka bukace shi ya bayyana a gaban wata kotu ya wanke kan shi daga zargin hannu a cikin abun fallasar sayen jarirai daga kasar Najeriya.

Wannan abun fallasar safarar jarirai ya rutsa da manyan jami'an kasar Nijer tare da iyalan su, a ciki har da ministan aikin gona Abdou Labo.

XS
SM
MD
LG