Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

VENEZUELA: Hukumomin Sun Musanta Yin Aringozon Kuri'u


 Nicolas Maduro
Nicolas Maduro

Shugaban kasar Venezuela da babban jami’in hukumar zabe jiya Laraba, suka musunta cewa an yi coge a adadin mutanen da suka fito kada kuria, da kara a kalla miliyan daya a zaben dake cike da tankiya da zai ba majalisa ikon sake rubuta kundin tsarin mulkin kasar.

Shugabar hukumar zaben ta kasa Tibisay Lucena tace irikirarin da wani kamfanin fasahar zabe na kasar Birtaniya yayi rashin sanin ya kamata ne, kuma tayi barazanar daukar matakin shari’a a kan kamfanin.

Lucena tace, wannan ra’ayi ne na kamfanin da rawar da ya taka kawai a zaben shine samar da tallafi ta fannin amfani da fasahar zamani da ba shi da wata alaka da sakamakon zaben.

Shugaban kamfanin Smartmatic na kasar Birtaniya, Antonio Mugica ya fada a birnin London jiya Laraba cewa, babu tantama, adadin kuri’un da aka sanar ba daidai bane. Sai dai bai bayyana ko murda kuri’un ya sauya sakamakon zaben da aka gudanar ranar Lahadi ba.

Shugaba Nicolas Maduro ya fada a jawabin da ya yi a tashar talabijin cewa, Amurka da Birtaniya ne suka matsawa Mugica lamba. Ya sake jaddada matsayin gwamnati cewa, mutane miliyan takwas suka kada kuri’a, ya kara da cewa ba domin masu zanga zanga sun toshe hanyoyi ba, da mutanen da suka kada kuri’a sun kai miliyan goma.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG