Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wai Ko Wa Ake Ganin Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A Nijar?


An cigaba da kidaya kuri'un da aka kada a karshen mako, don zaben sabon shugaban kasar jamhuriyar Nijar.

Tun bayan kammala zaben shugaban kasar jamhuriyar Nijar zagaye na biyu da aka yi a karshen makon nan, inda 'yan takara biyu da suka samu kuri'u mafi rinjaye a zagayen farko suka sake karawa, hankalin duniya yanzu ya koma kan kasar don samun sakamakon zaben,

Hukumar zaben jamhuriyar ta Nijar, ta sanar da cewar daga cikin da'irori 266 da ake da su a kasar, zuwa yanzy an kammala kidaya kuri'u na da'irori 197, haka na nuna cewar an kidaya fiye da kashi buyi cikin ukku na baki daya da'irorin da ake dasu a kasar baki daya.

Hukumar ta bayyana sakamakon da ke nuna cewar Muhammad Bazum shi ke kan gaba a baki dayan kurin'un da aka kada, sai abokin takarar shi Alh. Muhammad Usman, wanda ke biye da shi.

Ana sa ran samun takamaiman sakamakon da zai nuna wanda ya lashe zaben, nan da zuwa ranar Laraba da yamma. Sai ku cigaba da bibiyar shafukanmu don samun karin bayani akan sakamon zaben.

Ana iya sauraron wannan rahoton cikin sauti, inda Mahmud Lalo ya zanta da wakilin Muryar Amurka, Sule Munmuni Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:50 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG