Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Duk Da Yarjajjeniyar Da Aka Cimma A Sudan Ta Kudu, Ba a Sako Fursunan Yaki Ko Guda Ba.


Wani sabon rahoto na Majalisar Dinkin Duniya ya ce watanni shida bayan sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar 12 ga Satumba, shekarar 2018, har yanzu babu wanda aka sake daga cikin fursunonin siyasa wadanda suke tsare a Sudan ta kudu.

Biyu daga cikin manyan masu sukar gwamnati, Aggrey Idri, mamban kungiyar SPLM-IO, da Dong Samuel Luak, lauya mai kare hakkin bil adama sun bace a ranar 23 zuwa 24 ga watan Janairu, shekarar 2017, daga Nairobi.

Masana a Majalisar dinkin duniya kan harkokin kasar Sudan ta Kudu sun bayyana cewa, gwamnatin Sudan ta Kudu ta karyata cewa ta san inda Idri da Luak suke.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG