Daruruwan ‘yan Najeriya da ke neman takardun visar Amurka, ba su samu damar a saurare su ba a ofisoshin jakadancin kasar da ke Abuja da Legas sanadiyar takaddamar da ke tsakanin shugaba Donald Trump da ‘yan majalisar dokoki kan kasafin kudin tafiyar da ayyukan gwamnati.
Da yawa daga cikin ‘yan Najeriya a cewar jaridar Leadership, ba su iya zuwa ofisoshin ba saboda sun kasance a rufe.
Daga cikin wadanda lamarin ke shafa a cewar jaridar, akwai masu yawon shakatawa, ‘yan kasuwa, dalibai da sauransu.
Tun a ranar 22 ga watan Disamba, kudaden tafiyar da gwamnatin Amurka suka kare, inda aka gaza sabunta wasu kudaden, saboda shugaba Trump ya ki amincewa ya sa hannu a dokar da za ta ba damar samar da kudaden, saboda ba a saka kudin gina katanaga a tsakanin Amurka da Mexico dala biliyan 5 da ya nema daga majalisar ba.
A yau aka shiga yini na 11 da rufe wasu daga cikin ma’aikatun kasar, lamarin da ya kassara al’amura da dama ya kuma sa aka dakatar da dubun dubatar ma’aikata daga zuwa aiki.
Ko da yake, akwai wasu ma’aikatu da ayyukansu ke da muhimmancin da aka bari a bude, amma ma’aikatan suna aiki ne ba tare da ana biyansu ba.
Amma gabanin rufe ma'aikatun, majalisar dattawan ta amince cewa za a biya ma'aikatan kudadensu idan an sasanta.
A ranar Alhamis ake sa ran sabuwar majalisar wakilai za ta fara zamanta, ana kuma fatan za su amince da wata doka da za ta sa a fitar da kudaden tafiyar da gwamnati har zuwa watan Satumba, amma ba tare da kudaden gina katangar ba.
Rahotanni sun ce babu tabbacin wannan doka za ta karbu a zauren majalisar dattawa.