Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yadda Ziyarar Tawagar Da Buhari Ya Aika Sokoto Ta Kaya


Babban hafsan hafsoshin rundunar saman Najeriya Air marshall Sadique Abubakar
Babban hafsan hafsoshin rundunar saman Najeriya Air marshall Sadique Abubakar

Babban hafsan mayakan sama a Najeriya Air Marshall Sadiq Abubakar ya ziyarci Sokoto, domin nazarin abın da ya kamata a yi kan hare-haren da ake yawan kai wa a Sokoto.

A karshen makon da ya gabata ne ya kai ziyarar kuma daga isa jihar ya fara zuwa gidan sarkin Musulmi Muhammadu Sa'ad Abubakar na uku ne domin fara tattaunawa da shi.

A cewar Air Marshall Sadiq, "wannan aiki na samar da zaman lafiya, aiki ne da muka riga muka fara a Zamfara da Katsina, yanzu kuma za mu soma shi ne a Sokoto."

Mai alfarma Sarkin Musulmin dai ya yi na'am da wannan matakin, kuma ya ce idan aka samar da kayan aiki, tabbas za a fi karfin 'yan ta'addan.

A cewar wata tawagar da aka nada domin gano yawan mutanen da suka rasa rayukansu a hare-haren kwannakin nan kadai, mutanen sun kusan kai 100.

Ko a karshen makon da ya gabata dai sai da aka sake kai wani hari a kauyen Gatawa wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka biyu, aka kuma sace wasu mutum biyu.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG