Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yadda Ziyarar Tawagar Da Buhari Ya Aika Sokoto Ta Kaya


Babban hafsan hafsoshin rundunar saman Najeriya Air marshall Sadique Abubakar

Babban hafsan mayakan sama a Najeriya Air Marshall Sadiq Abubakar ya ziyarci Sokoto, domin nazarin abın da ya kamata a yi kan hare-haren da ake yawan kai wa a Sokoto.

A karshen makon da ya gabata ne ya kai ziyarar kuma daga isa jihar ya fara zuwa gidan sarkin Musulmi Muhammadu Sa'ad Abubakar na uku ne domin fara tattaunawa da shi.

A cewar Air Marshall Sadiq, "wannan aiki na samar da zaman lafiya, aiki ne da muka riga muka fara a Zamfara da Katsina, yanzu kuma za mu soma shi ne a Sokoto."

Mai alfarma Sarkin Musulmin dai ya yi na'am da wannan matakin, kuma ya ce idan aka samar da kayan aiki, tabbas za a fi karfin 'yan ta'addan.

A cewar wata tawagar da aka nada domin gano yawan mutanen da suka rasa rayukansu a hare-haren kwannakin nan kadai, mutanen sun kusan kai 100.

Ko a karshen makon da ya gabata dai sai da aka sake kai wani hari a kauyen Gatawa wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka biyu, aka kuma sace wasu mutum biyu.

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG