Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Banga Da Mafarauta Sun Sami Horon Cudanya Da Al’umma


A ci gaba da neman mafita ga matsalar tsaro a Nijeriya, Majalisar dinkin duniya, karkashin shirin taimakawa kasashe masu tasowa, ta horadda ‘yan kato da gora, ‘yan banga da mafarauta.

Majalisar ta koyar da su dabarun cudanya da al’umma da hada kai da jami’an tsaro, don samun mafita kan matsalar tsaro a Arewa maso gabashin Najeriya.

Matasa dari hudu ne daga jihohin Adamawa da Yobe, suka zo cibiyar koyar da dabarun shugabanci da zama dan kasa na gari a Jos jihar Filato.

An horar da su yadda zasu kaucewa take hakkin dan adam, fahimtar darajar al’adun al’umma da hadin kai wajen gudanar da aikinsu ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

Ga cikakken Rahoton cikin sauti daga Zainab Babaji a Jos.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:34 0:00
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG