Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Bindiga Sun Bude Wuta Akan Tawagar Majalisar Dinkin Duniya


Tawagar Majalisar Dinkin Duniya
Tawagar Majalisar Dinkin Duniya

An saki jami'an Majalisar Dinkin Duniya bayan da wasu 'yan bindigar suka kama su a Libya, kasar dake fama da rikicin siyasa tun bayan da aka hambarar da gwamantin tsohon shugaban kasar marigayi Moammar Ghaddafi.

Wasu ‘yan bindiga sun budewa wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Libiya wuta jiya Laraba, sun kuma kama wakilan Majalisar ta Dinkin Duniya su bakwai.

Wani mai magana da yawun MDD ya ce tawagar na tafiya ne tsakanin birnin Tripoli da garin Surman a yammacin Libya yayinda ‘yan bindigar suka fara harbinsu. Sun lalata daya daga cikin motocin tawagar, amma jami’a 7 da suka kama na dan lokaci, sun sake su ba tare da yi musu wani lahani ba.

MDD ta godewa jami’an gwamnatin Libya da hukumomin yankin don kokarin da suka yi na tabbatar da cewa sun kare jami’an. Majalissar ta kuma ce jami’anta dake Libya za su cigaba da goyon bayan zaman lafiya da tsaro a kasar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG