Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu 'Yan Binidga Sun Kashe Sojoji Da Dansanda A Jihar Bayelsa


Hoton wasu 'yan binidga cikin jiragen ruwa.
Hoton wasu 'yan binidga cikin jiragen ruwa.

Rundunar kiyaye zaman lafiya ta musamman JTF a yankin ta tabbatar faruwar lamarin.

Runudunar tsaro ta musamman JTF a yankin Niger Delta, ta tabbatar da rahotanni da suke fitowa daga yankin cewa wasu 'yan binidga sun kai hari cikin karamar hukumar Nembe suka kashe sojoji hudu da Dan sanda daya.

Wakilin Sashen Hausa a yankin Lamido Abubakar Sakkwato, ya gayawa Bello Galadanci cewa yanzu jami'an rundunar tsaro ta JTF tana kan hanyarta zuwa jihar Bayelsa inda lamarin ya auku.

Zuwa yanzu dai hukumomi basu bada karin bayani ko akwai wadanda suka jikkata sakamakon harin na yau ba.

Tun dai bayan canjin gwamnati ake samun rahotannin cewa 'yan bindiga a yankin suna yunkurin sake komawa fagen daga. A makonni da suka wuce sai da jami'an tsaro suka kai somame suka damke mutane da ake zargi suna shirin kai hare hare a yankin.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00

XS
SM
MD
LG