Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Kwamitin da Zai Binciki Kamfanin NNPC Zai Yi Zaman Farko


Kamfanin NNPC
Kamfanin NNPC

Kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya da ta kafa a karkashin shugabancin Senata Aliyu Magatakardan Wamako domin ya binciki badakalar da ake zargin an tafka a kamfanin NNPC zai fara zamansa yau

Shugaban kwamitin binciken, Senata Aliyu Magatakardan Wammako, a zantawar da yayi da wakilinmu Saleh Shehu Ashaka ya bayyana hakan.

Shugaban kwamitin yace, a zamansu na yau ne zasu tantance tsarin aikin da aka basu da kuma yadda zasu gudanar da shi.

Dangane da cewa ko an kafa kwamitin din ne domin a ci wa wasu zarafi, Senata Aliyu yace ba za’a yi anfani dasu ba a muzgunawa wani,zasu yi aikin ne tsakaninsu da Allah, ta yadda zasu taimakawa Shugaba Muhammad Buhari a yakin da yake yi da cin hanci da rashawa.

Ga rahoton Saleh Ashaka da karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:47 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG