Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Ta Ke Ranar Jaddada Zaman Lafiya Tsakanin A'umma


Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon
Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon

Yau, ranar jaddada zaman lafiya tsakanin al'ummomin duniya, Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ban Kimoon ya yi kira ga kasashen duniya da su hada kai wajen tabbatar da zaman lafiya. Wasu 'yan Nijeriya ma sun bayyana ra'ayoyinsu game da wannan ranar.

Yau ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don jaddada muhimmancin zaman lafiya tsakanin al’umma. Wakilin Muryar Amurka a birnin Ibadan, Hassan Ummaru Tambuwal ya ruwaito Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Mr. Ban Ki-moon na kira ga kasashen duniya da su hada kai wajen tabbatar da zaman lafiya tsakanin al’umma.

Wakilinmu a birnin Ibadan na jihar Oyo, Hassan Ummaru Tambuwal ya ruwaito wani mai suna Abarshi a kasuwar Shanu da ke Ibadan na cewa ya na da kyau da Majalisar Dinkin Duniayar ta ware wsannan ranar, to amma zaman lafiya bai yiwuwa muddun babu zaman adalci. Y ace yakamata a inganta asibitoci da makarantu da sauran abubuwan da talaka ke amfana da su muddun ana son hankalin jama’a ya kwanta.

Shi ma wani mai suna Abdullahi y ace fatansa shi ne a samu zaman lafiya a arewa maso gabashin Nijeriya da ma duniyar baki daya. Shi kuwa Suleiman Umar kira ya yi da cewa albarkacin wannan ranar Shugabanni su yi rungumi akidar aldalci don a zamu zaman lafiya mai dorewa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:30 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG