WASHINGTON, DC —
Nan zuwa daren yau talata, za a san ko wacece a tsakanin Real Madrid da Bayern Munich zata kai labari zuwa ga wasan karshe na cin kofin zakarun kulob-kulob na Turai. Yanzu haka ‘yan Real Madrid su na can birnin Munich, domin kare ci daya da babun da suka yi ma zakarun na Jamus a karawarsu ta farko a makon jiya.
Wani abin murna ga ‘yan Real Madrid shi ne cewa da alamun ciwon da zakaransa Cristiano Ronaldo ya ji a kafa ya warke, domin a karshen mako, ya buga wasan minti 60, har ya jefa kwallaye biyu a wasan lig da suka buga da Osasuna.
Idan har Real ta jefa koda kwallo guda ne a raga a wasan yau, to fa tilas sai Bayern ta jefa kwallaye har uku kafin ta iya shigewa. Masana tamaula su na hasashen cewa zai yi wuya Bayern, wadda a baya-bayan na ta fara yin tuntube, ta jefa kwallaye har uku a ragar Real Madrid.
Za a fara wannan wasa da karfe 7:45 na daren yau talata agogon najeriya.
A gobe dai za a buga wasa na biyu a tsakanin Chelsea da daya kungiyar ta Madrid, Atletico. Za a buga wasan karshe na cin kofin zakarun kulob na Turai na bana a birnin Lisbon ta kasar Portugal a ranar 24 ga watan Mayu.
Wani abin murna ga ‘yan Real Madrid shi ne cewa da alamun ciwon da zakaransa Cristiano Ronaldo ya ji a kafa ya warke, domin a karshen mako, ya buga wasan minti 60, har ya jefa kwallaye biyu a wasan lig da suka buga da Osasuna.
Idan har Real ta jefa koda kwallo guda ne a raga a wasan yau, to fa tilas sai Bayern ta jefa kwallaye har uku kafin ta iya shigewa. Masana tamaula su na hasashen cewa zai yi wuya Bayern, wadda a baya-bayan na ta fara yin tuntube, ta jefa kwallaye har uku a ragar Real Madrid.
Za a fara wannan wasa da karfe 7:45 na daren yau talata agogon najeriya.
A gobe dai za a buga wasa na biyu a tsakanin Chelsea da daya kungiyar ta Madrid, Atletico. Za a buga wasan karshe na cin kofin zakarun kulob na Turai na bana a birnin Lisbon ta kasar Portugal a ranar 24 ga watan Mayu.