Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yayin da 'Yan Gudun Hijira Ke Kwarara Zuwa Mubi Cutar Kwalara ta Bullo


Yadda 'yan gudun hijira kan yi ta jele
Yadda 'yan gudun hijira kan yi ta jele

Dubban 'yan gudun hijira suna kwarara zuwa garin Mubi dake arewacin jihar Adamawa lamarin da yanzu ya haddasa bullar cutar kwalara wadda ta kashe mutane da dama.

Kawo yanzu kimanin mutane biyar ko bakwai ne suka rasu sanadiyar cutar ta kwalara.

Ana kiran gwamnanti ta gaggauta ta taimaka da magani domin kada wadanda basu kamu ba yanzu su kamu nan gaba. Banda wadanda suka kamu da cutar kwalaran akwai mata masu juna da dama da wasu goma sha takwas da suka haihu dake bukatar kula.

Akwai yankunan Borno da Adamawa dake hannun 'yan Boko Haram yanzu. Wasu ma dake Madagali cikin jihar Borno sun kauracewa gidajensu suna kwana a dazuka domin mamaye garin da 'yan Boko Haram suka yi.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:18 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG