Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za'a Gabatarwa Majalisar Dinkin Duniya Bayani Game da Farmakin Da Aka Kai Kan Musulman Rohinga


myanmar hau do suan
myanmar hau do suan

Yayinda ake shirin gabatar da bayanin, shi kuma jakadan Myanmar a majalisar Dinkin Duniya bai yi na'am da wannan taron daza ayi ba yana ganin bashi da wani amfani.

Wani kwamiti na musamman da Majalisar Dinkin Duniya ta kafa¸ wanda ya zargi sojojin kasar Myanmar da aikata kisan kiyashi akan musulmai ‘yan Rohinga a shekarar da ta gabata, na shirin yiwa kwamitin sulhun majalisar bayani.

Kasashe tara ne daga cikin mambobi goma sha biyar na kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya, suka nemi a gana da shugaban kwamitin a hukuman ce, a cikin bukatar da suka mika shekaranjiya Talata.

Sai dai kuma jakadan Myanmar a Majalisar Dinkin Duniya, Ambasada Hau Do Suan, ya nuna adawa da taron a wata wasika da ya aike ranar talata, inda yace ba wani abinda taron zai tsinana.

A wani rahoto da aka fitar a watan Agustan da ya wuce, kwamitin binciken ya ce ya gano hujjoji da suka nuna yanda sojojin Myanmar suka gudanar da kisan kare dangi akan musulman Rohingya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG