Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za A Kafa Rundunar JTF A Zamfara


ZAMFARA: Jirgin yaki
ZAMFARA: Jirgin yaki

Gwamnatin jihar Zamfara ta dauki matakin shawo kan matsalar tsaro da ta addabi jihar, sakamon ci gaba da kai hare hare da garkuwa da jama'a da ake fuskanta.

Duk da rundunonin soji tare da jiragen yaki da gwamnatin tarayyar Nijeriya ta tura a jihar Zamfara, ana ci gaba da samun yawaitar ayyuka ‘yan bindiga, kama daga kai hare-hare, da kisan jama’a, har ma da satar mutane domin karbar kudin fansa, wanda a yanzu ya zama ruwan dare a jihar.

To sai dai gwamnan jihar Abdul aziz Yari Abubakar, ya ta’allaka wannan yanayin da rashin iya game dukkan yankunan jihar a lokaci daya da jami’an tsaron, duk kuwa da yawan da suke da shi.

A kan haka ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki akan sha’anin tsaro a Gusau babban birnin jihar, Gwamna Yari ya bada sanarwar matsayar da aka cimma ta kafa rundunar hadin gwiwa da farar hula, wato “Civilian JTF” a turance, a karkashin jagorancin hukumomin tsaro a jihar.

Tuni da aka yi haramar samar da dokar kafa sabon tsarin a majalisar dokokin jihar, inda za’a dauki matasa kusan 8,500 da za’a horar da su, tare kuma da biyansu alawus na naira 15,000 a kowane wata, kari ga alkawarin bada tukuicin naira miliyan daya ga duk wanda ya kama dan ta’adda mai bindigar AK47.

Saurari cikakken rahoton Murtala Faruk Sanyinna:

Za a kafa rundunar JTF a Zamfara-3:13"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:14 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG