Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben Kamaru: Maurice Ya Ce Shi Ya Ci, Ba Paul Biya Ba


Shugaba Biya
Shugaba Biya

Ga dukkan alamu, idan ba a kai zuciya nesa ba, za a shiga rudu a kasar kamaru sanadiyyar takaddamar bayan zaben Shugaban kasa. Wannan ko ya biyo bayan cewa da wani dan adawa ya yi shi ya ci zaben Shugaban kasa, duk kuwa da bai gabatar da hujja ba.

Da alamar dai wata kura na gab da tashi a kasar Kamaru, inda tsohon Ministan Shari’ar Kasar kuma dan takarar Shugaban kasa na jam’iyyar MRC, Maurice Kamto, ya ce shi ne ya ci zaben Shugaban kasar, ba Paul Biya ba, al’amarin da ya janyo martanin hiukumomin kasar.

Wani jami’I a Kotun Kundin Tsarin Mulki ta kasar Kamaru, Suleiman Alhaji, ya ce bai dace Mr. Maurice ya yi gaban kansa wajen ayyana kansa a matsayin dan takara ba. Haka zalika, Ministan Yada Labaran kasar, Isa Ciroma, y ace Maurice ya saba ka’ida.

Ga wakilinmu, Awwal Garba da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG