Kungiyar Kwadago Ta Najeriya Ta Gudanar Da Zabe

kungiyar kodako a Najariya

Kungiyar Kodago Ta Kasa A Najeriya Ta Zabi Sabbabin Shugabanni bayan an shafe kwanaki biyu ana yakin neman zabe da kada kuri'a.

Kungiyar Kodago ta kasa a Najeriya ta kammala taron kolinta tare da zaben sabbabin shugabanni

Wakilinmu Nasiru Adamu el-Hikaya ya ruwaito cewa, an zabi sababbin shugabannin ne bayan an shafe kwana biyu ana kadawa da kirga kuri'u bayan neman goyon baya da janyewar wadansu 'yan takara.

Daga karshe aka zabi Ayuba Wamba wani tsohon shugaban kungiyar ma'aikatan jinya a matsayin sabon shugaba.

Dai dai wadansu da basu gamsu da wadansu jami'an da aka zaba ba, sun ce wadansu daga cikin sababbin shugabannin basu cancanci rike mukaman ba sabili da rashin gaskiya da suka nuna a mukaman da suka rike a lokutan bayan.

Ga cikakken rahoton.

Your browser doesn’t support HTML5

Zaben Kungiyar Kodago A Najeriya-2:02