Yakubu Dogara Ya Zamo Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Nigeria National Assembly

Dan majalisar wakilai Yakubu Dogara daga mazabar Tafawa Balewa da Bogoro a Jihar Bauchi, ya zamo sabon kakakin majalisar wakilan tarayya ta Najeriya.

Yanzun nan aka rantsar da dan majalisar bisa wannan mukami, a bayan da aka zabi Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattijai ta Najeriya.