Kotun Daukaka Kara Ta Ce Gawuna Ne Ya Yi Nasara, Abba Aka Ci Tara

Nasiru Yusuf Gawuna

Biyo bayan rudamin da ya karade kafafen sada zumunta game da shari’ar zaben gwamnan jahar Kano, mai nasaba da jita jiyar da aka yada cewa an yi kuskure wajen yanke hukuncin daukaka kara, Kotun Daukaka Kara da ke Abuja, ta yi watsi da jita jitar. Ta fitar da kofin takardar hukuncin baya bayan nan, wanda ya sha banban da kwafin da aka yi ta yadawa ta kafar sada zumunta tun daga jiya.

Bisa ga kwafin da Kotun Daukaka karar ta fitar yau, gwamna Abba ne aka ci tarar naira miliyan daya. An kuma yi watsi da karar da ya daukaka.

Ga Mahmud Ibrahim Kwari da cikakken rahoton:

Your browser doesn’t support HTML5

Kotun Daukaka Kara - Gawuna Ne Ya Yi Nasara.mp3