A Masar Kotu Ta Sallami Ba-Amurkiya Daga Gidan Yari

Wata kotun Masar ta sallami wata ba-Amurkiya 'yar asalin Masar tare da wasu mutane 7, bayan kasancewa a daure na kusan tsawon shekaru uku saboda zargin safarar mutane ta wajen amfani da wata kungiyarta mai da'awar taimakon yaran da ke kan titin Alkhahira.

Babbar wadda ake tuhumar, Aya Hijazi, da mijinta da kuma wasu mutane 6 sun kasance cikin fursuna tun daya watan Mayun 2014, lokacin da 'yan sanda a birnin Alkhahira su ka kai samame kan gidauniyarta ba tare da wata takardar sammaci ba, su ka kwace kananan komfutoci da sauran na'urori.

An tuhumi mutane 7 din ne da laifin safarar mutane, da kuma lalata da yara kanana, da kuma biyan yara kudi su shiga zanga-zangar kyamar gwamnati. Kama su da aka yi ya janyo korafe-korafe daga kungiyoyin raji da dama, wadanda su ka ce zarge-zarge an kago ne kawai, kuma wani bangare ne na yadda gwamnati ke kokarin murkushe kungiyoyin sa kai.