Amurka Zata Kafa Sansanin Sojoji a Kasar Nijar

Predator [file photo]

Har yanzu hukumomin Jamhuriyar Nijar, basu ce komai ba kan sabunta wani sansanin Sojojin kasar Amurka.

Har yanzu hukumomin Jamhuriyar Nijar, basu ce komai ba, kan sabunta wani sansanin Sojojin kasar Amurka, da tace zata girke Sojojin ta, a arewacin kasar ta Nijar.

Kafofin yada labarai na Amurka da sauran wasu na duniya na yada labarai cewa Amurka, zata sabunta wani sansanita daga Birnin Yemai zuwa yankin Agadas dake arwacin kasar ta Nijar.

Tun farkon shekaran data gabata ne hukumomin kasar Nijar, suka amince da kasancewar dakarun kasashen yamma ciki harda Amurka, a kasar ta Nijar.

Kawo yanzu rahotanin na cewa kimanin Sojojin Amurka, dari da ashirin ne ke girke a sassa daban daban na jamhuriyar Nijar.

Your browser doesn’t support HTML5

Amurka Zata Kafa Sansanin Sojoji a Kasar Nijar - 3'12"