An Kaddamar Da Sabon Sansanin Sojin Najeriya a Birnin Gwari

Rundunar sojojin saman Najeriya ta kaddamar da wani Sabon sansani a Birnin Gwari, tare da tura jiragen yaki a yankin don sake sabon damarar ci gaba da tunkarar ta'addancin 'yan bindiga dadi.

Babban Hafsan Hafsoshin Rundunar sojojin saman Najeriya Air Marshall Sadique Baba Abubakar ya ce, sun kuma tura jiragen yakin nan da Najeriya ta sayo daga kasar Italiya don wannan aiki.

Babban Hafsan sojojin saman Najeriyar ya ce, sun kuma tura karin bataliyar mayakan sama na musamman wato "special forces" da za su yi aiki daga kasa, duk dai a kokarin cimma yan ta'addan.

Sadique Abubakar ya ce sojojin saman Najeriya za su yi ta yakar 'yan bindigar har sai sun tabbatar da tsaro a yankin na Birnin Gwari da ma sauran shiyyar Arewa Maso Yamma.

A cewar mai sharhi kan sha'anin tsaro Mohammed I. Usman, irin wannan hobbasar lalle ka iya 'yin tasiri sosai wajen kawo karshen 'yan bindigar.

Ga wakilinmu Hassan Maina Kaina da cikakken rahoton:

Your browser doesn’t support HTML5

Rundunar Sojojin Saman Najeriya Ta Kaddamar Da Sabon Sansani A Birnin Gwari 02'23"