Hedkwatar rundunar tsaron Najeriya ta yi karin haske kan hoton da wasu ke ta sake yadawa a shafukan sada zumunta na shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Doguwa, dauke da wata bindigar soji kirar AK47, inda wasu sojoji ke gwada mai yadda ake harbawa a cikin wani Daji.
Yayin da ake daf da gudanar da zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohi a Najeriya, jama’a na kara nuna damuwa kan sha’anin tsaro a lokacin zaben.
Babban kwamandan rundunar dakarun kawancen yankin tafkin Chadi Manjo Janaral Abdul Kalifa Ibrahim da kuma ake kira AK, ya yi wa Muryar Amurka karin haske kan cafke 'yan kungiyar Boko Haram sama da dari takwas da suka yi a baya-bayan nan.
A wani mataki na tunkarar ta'addanci a yankin Tafkin Chadi ta dukkannin bangarori, rundunar kawancen yankin wato MNJTF ta matsa kaimi wajen afkawa ba kadai kan ‘yan ta'addan ba, har da karin samame akan fararen hular da ke taimakon ‘yan ta'addan wajen samar masu da kayayyaki ko bayanai.
Hukumar tsaron farin kaya ta DSS a Najeriya ta ce ta gano wani shirin boye da wasu mutane ke yi don kawo rudu da tabarbarewar doka da oda a kasar jim kadan bayan gudanar da zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da aka shirya yi ranar 11 ga watan Maris.
Rundunar Sojin Najeriya ta kaddamar da bincike kan wani jami'inta da ya bindige dan uwansa soja kana shi ma ya bindige kansa a wani sansanin sojoji dake Rabah a Jihar Sokoto.
Gwamnatin Najeriya ta aike da tallafin dalar Amurka miliyan daya ga al'ummar kasar Turkiya, a wani matakin saukaka masu irin radadin da ibtila'in da girgizar kasa ta janwo masu.
Jama’a masu zaman jiran sakamakon zaben da aka gudanar ne jiya Asabar 25 ga Fabrairun 2023.
Shugaban Amurka Joe Bide ya ce ya yaba wa yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi a Najeriya, da ta samu sanya hannun jami’iyyun siyasa da ‘yan takara da zasu fafata a zaben shugaban kasar a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Jakadan kasar Canada a Najeriya Mr. Jammie Christoff ya bayyana hakan ne yayin da ya ke magana a wani taron hadin gwiwa tsakanin Najeriya da kasar ta Canada, don karfafa matakan hadin kai na tunkarar kalubalen safarar mutane da yin kaura ba bisa ka’ida ba.
Taron na manyan Hafsoshin Sojojin da sauran shugabannin hukumomin tsaron kasar na zuwa ne a daidai lokacin da mayakan Boko Haram suka saki wani faifan Video wanda a ciki suke barazanar kawo cikas yayin zaben.
Babban bankin Najeriya (CBN) ya karyata labarin cewa ya umarci bankuna a kasar da su fara karbar takardun kudi na Naira dari biyar da Naira dubu daya.
Shuganan hukumar zaben Najeriyar ya bayyana cewa tun a watan Fabrairun shekarar da ta gabata ne suka fidda wasu jerin ababe guda goma sha hudu da bisa doka dole sai an kaddamar dasu don tabbatar da ingancin zaben
An fara samun karin bayani game da mummunan farmakin da jiragen yakin mayakan saman Najeriya suka kai a sansanin mayakan Boko Haram dake dajin sambisa da safiyar yau asabar, inda suka babbake sansanin biyo bayan ruwan boma bomai da rokoki.
“Amurka ta ce ba ta goyon bayan kowane ‘dan takara a zaben Najeriya. Ta ce ita dai babban muradinta shi ne ta ga an gudanar da ingantaccen zabe, na gaskiya mai cike da adalci, wanda kowa da kowa zai na'am da shi”
“Ana dai zargin sojojin da danne hakkin dan Adam ciki har da zubar da cikin mata fiye da dubu goma da ake zargin Boko Haram sun yi wa Fyade”
Wani bene mai hawa uku ya ruguje a unguwar Gwarinpa da ke Abuja babban birnin Tarayyar Najeriya.
Wata babbar kotu a birnin Kaduna ta umarci hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya wato DSS da ta gaggauta gurfanar da mawallafin jaridar Desert Herald Malam Tukur Mamu a gaban kotu.
Birgediya Janaral Tukur Isma'il Gusau, sabon kakakin hedikwatar rundunar tsaron Najeriya, ya amshi ragamar aiki daga hanun darakta mai barin gado, Manjo Janaral Jimmy Akpor.
A kokarin kawo karshen aika aikar 'yan ta'addan Boko Haram da ISWAP a yankunan kasashen tafkin Tchadi, dakarun kawancen kasashen yankin na can na ci gaba da fatattakar 'yan ta'addan a baki dayan yankin cikin wani farmaki ba kakkautawa da ma sintiri da ake yi akai akai.
Domin Kari