Tafkin Chadi, dake da murabba’in kadada dubu dari biyar a shekaru hamsin baya, yanzu ya ragun da kimanin kashi, tamanin cikin dari.
Sakataren, hukumar dake kula da tafkin Injiniya, Sanusi Imam Abdullahi, ne ya bayana a hiran da suka yi da babban editan muryar Amurka, Aliyu Mustapha, a birnin Washington.
Injiniya, Imam Abdullahi, yace gwamnatin Amurka da hukumomin dake kula da tsaron nahiyar Afirka, ne suka gudaner ta taron da ya halarta domin tsaro da ruwa a Afirka, wanda aka gudanar a Washington.
Ya kara da cewar rashin tsaro a yankin tafkin Chadi, ya hana mutane wal-wala kamar yanda aka saba, kimanin kasashe takwas ne da Amurka, suka halarci taron akan ruwa da tsaro.
Your browser doesn’t support HTML5