Wani hari da aka kai a yau Alhamis a gabashin Pakistan ya kashe a kalla mutane takwas kuma ya jikata wasu mutane 20.
WASHINGTON DC —
Pashewar ya faru ne a wata kasuwar masu hannu da shuni a cikin birnin Lahore.
Jami’ai sun ce ba’a gano dalilin pashewar nan da nan ba
Pashewar ya faru ne, wuni guda bayan Pakistan ta kaddamar da ayyukan soji a fadin kasar a karon farko, don kawar da barazanan ayyukan yan ta’adda.
Pakistan ta samu karuwan hare haren kunar bakin wake da na ‘yan bindiga cikin kwana kwanan nan da suka yi sanadiyar kashea kalla mutane 130 .