Izala ta Shawarci Musulmi su Nemi Ilmin Zamani Dana Addini

'Yan mata musulmi.

Kungiyar tayi wannan kiran ne a wani gangamin wa'zi da ta shirya a birnin Abuja.
Daga Abujan Najeriya mun sami rahoton cewa kungiyar Izalatul Bidi’a wa ikamatus sunna ta kasa, tayi kira ga jama’ar musulmi su tashi haikan wajen neman ilmin zamani, domin kamar yadda shugabannin kungiyar suke cewa “Boko Halal ne”.

Kungiyar tayi wannan kiran ne a wani gangamin wa'azi data shirya a babban birnin Najeriya.Inda aka yi bikin kaddamar da littafin da wani shugaban kungiyar ya rubuta kan muhimancin neman ilmin zamani.

Ga karin bayani.

Your browser doesn’t support HTML5

Boko Halal