PDP Ta Kafa Kwamitin Duba Batun Danbaba Suntai

Johns Hopkins School of Medicine

A karon farko uwar jam'iyar PDP mai mulkin Najeriya ta saka baki a maganar shugabancin jahar Taraba
Al’ummar jahar Taraba ta yi bikin ranar Demokradiya cikin murna da farin ciki saboda samun labarin cewa uwar jam'iyar PDP ta kafa kwamitin duba lafiyar gwamna Danbaba Suntai wanda watanni kusan shida kenan ya na jinya sanadiyar hatsarin jirgin saman da ya ke tukawa shi da kan shi. Jam’iyar ta PDP ta kafa kwamitin ne da zummar nada mukaddashin gwamnan jihar Alhaji Garba Umar a matsayin gwamna mai cikakken iko. Ga dai wakilin Sashen Hausa Ibrahim Abdulaziz da karin bayani.

Your browser doesn’t support HTML5

PDP ta kafa kwamitin tantance halin da gwamna Danbaba Suntai ya ke ciki - 2:04