Saudiyya Ta Yi Wa Ma'aikatar Tsaronta Garambawul

Dakarun Saudiyya

Sarki Salman na Saudiyya ya yiwa wasu manyan sojojin kasar da ministoci garambawul, a wani gagarumin sauyi da ya aiwatar a fannin tsaron kasar.

Yau Talata kafar labarai ta Saudiyya ta fitar da rahotan dake cewa, Sarkin ya canza hafsoshn sojan sama da na ‘kasa tare da kuma wasu jigagan jami’an ma’aikatar harkokin cikin gida.

Haka kuma saudiyya ta sanar da nada mace ta farko a matsayin mataimakiyar misintan ayyuka da ci gaban kasa, a wani yunkuri na saka mata harkokin aiki a kasar.

Ta kuma bayyana shirinta na samar da sauyi a ma’aikatar tsaron kasar ba tare da yin cikakken bayani ba.