Siyasar Jihar Adamawa Ta Dauki Sabon Salo

ADAMAWA: Gwamna da mataimakinsa

Wasu kusoshin jam’iyar ne dake tare da bangaren su Murtala Nyako,Nuhu Ribadu,Engr Markus Gundiri, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Babachur David Lawal, suka garzaya Abuja domin mika kukarsu na a sauke shugabanin jam’iyar na jihar, biyo bayan kalaman da shugaban jam’iyar Ibrahim Bilal yayi na cewa su ba wani dan takarar gwamna da suka sani sai gwamnan jihar Sen.Muhammadu Bindo Umaru Jibrilla.

To ko me yayi zafi haka? Mr Adamu Kamale, dan majalisar wakilai yace, muddin uwar jam’iyar ta rusa shugabanin jam’iyar, to fa labudda zasu sauya sheka su da sauran magoya bayan gwamnan zuwa wata jam’iya.

Wannan takaddamar dai na ko zuwa ne, yayin da shugabanin jam’iyar ta APC ke lashe aman da suka yi tun farko, inda suka fitar da wata sanarwar gaggawa domin fayyace matsayin game da yan takarar gwamnan.

Ga rahoton Ibrahim Abdulaziz..

Your browser doesn’t support HTML5

Siyasar Jihar Adamawa Ta Dauki Sabon Salo- 3'27"