Sojoji Sun Fatattaki 'Yan Boko Haram Daga Damaturu

Sojoji

Jami’an tsaro, a Damaturu babban birnin jihar Yobe sun fatattaki, ‘yan bindiga, da ake zato 'yan kungiyar Boko Haram ne, da suka yiwa garin Damaturu.

Jami’an tsaro, a Damaturu babban birnin jihar Yobe sun fatattaki, ‘yan bindiga, da ake zato 'yan kungiyar Boko Haram ne, da suka yiwa garin Damaturu, diran, mikiya da sanyin safiyar yau litinin.

Rahotanin na nuni da cewar an farma ‘yan bindigan ne, ta sama da kasa inda Sojoji suka fatattake ‘yan bindigar da ake zaton cewa ‘yan Boko Haram ne.

Da sanyin safiyar yau ne suka farma Jami’ar, jihar Yobe, rahotanin sun na nuni da cewa ‘yan kungiyar ta Boko Haram sun shigo garin Damaturu, ne ta kudu ta hanyar Gujjuba.

Koda yake jama'ar garin Damaturu a wannan karo sun yabawa jami'an tsaro saboda sunyi rawar gani wajen fatattakar 'yan kungiyar Boko Haram, daga Damaturu.

Your browser doesn’t support HTML5

An Fatattaki 'yan Boko Haram - 2"10"