Tarayyar turai, Birtaniya da Amurka Sun Yaba Da Zaben Osun

A cikin sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, Tarayyar turai, Birtaniya da Amurka, sun yaba da yadda aka yi zaben gwamnan jihar Osun duk da dai ba a kammala ba.

Sanarwar ta kuma yabawa hukumar zaben Najeriya bisa yadda ta inganta yanayin zabe da ma irin hobbasan da jami'an tsaro sukayi. Ta kuma yi kira ga duk masu ruwa da tsaki da su tabbatar da cewa an kammala zaben cikin lumana cikin gaskiya da adalci yayain da hukumar zabe ta kasa zata kammala gudanar da zaben a mazabu 7 wadanda basu samu damar kada kuri'unsu ba.

Hukumar zaben Najeriya ta bayyana kudrinta na kammala zaben cikin gaskiya da adalci.

Saurari Rahoton Hassan Maina K

Your browser doesn’t support HTML5

arayyar turai, Birtaniya da Amurka Sun Yaba Da Zaben Jihar Osun- 1"18


aina..