Taron Faransa Ya Amince Libya Ta Yi Zabe A Karshen Shekara

Taron kasashe 20 akan Libya da aka yi a Faransa

Jiya Talata kasashe ishirin suka yi taro a Paris babban birnin Faransa inda suka amince kasar Libya ta gudanar da zaben kasa a karshen wannan shekarar da zai samar da gwamnati daya ga kasar domin zaman lafiya da sake kafa kasar

Jagorar bangarori da kuma jami'an diflomasiyya daka kasashe sama da 20 da su ka yi taro jiya Talata a Birnin Paris sun cimma amincewa bisa manufa cewa kasar Libiya ta arewacin Afirka ta gudanar da zabe a karshen wannan shekarar.

Wannan taron shi ne karo na biyu da Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi yinkurin kawo zaman lafiya a Libiya.

Macrone ya yaba da matsayar da aka cimma, ya na mai cewa wani gagarumin cigaba ne a yinkurin da ake yi na samar da zaman lafiya a Libiya. "Yanzu dai ta bayyana cewa mun dukufa wajen taimakomn wannan kasar, da kuma jadawalin gudanar da zabukan majalisar dokoki da kuma na shugaban kasa" a cewarsa.

Shugaban gwamnatin "hadin kai" wadda kasashen duniya ke goyon baya mai mazauni a birnin Tripoli, Fayez al-Sarraj, dan shekaru 75 da haihuwa da Khalifa Haftar, wanda dakarunsa su ke da karfi a gabashin kasar, da kuma Kakakin Majalisar dokokin kasar da ke garin Tobruk na gabashin kasar sun cimma amincewa cewa Libiya ta gudanar da zabe ranar 10 ga watan Disamba, a cewar jami'an kasar Faransa.