Yarinyar da Aka Sace ta Koma Gida Kano

  • Aliyu Mustapha

'Yansanda

Wata yarinya da aka sace daga Kano, aka kaita Fatakwal tayi sa’ar dawowa gida lami lafiya
Wata yarinya mai suna Amina, ‘yar shekaru 15, da aka sace ta daga Kano dake arewancin Nigeria, a ka kaita Fatakwal ta jihar Rivers dake kudancin kasar, ta dawo gida lami lafiya, bayan tayi kamar mako daya ana nemanta a gidansu dake Kano. Yarinyar tace wasu mutane biyu ne suka yi awon gaba da ita lokacinda ta je sayen katin waya. Aliyu Mustaphan Sakkwato ya zanta da ita da kuma mahaifinta Alhaji Hamisu Abba kan wannan lamarin – da kuma yadda aka yi har ta dawo gida:

Your browser doesn’t support HTML5

Yarinyar da Aka Aace ta Koma Gida Kano - 5:04