Yaya Jama'a Suka Ji Korar Gulak?

Shugaba Goodluck Jonathan, wanda ya kori Ahmed Gulak.

​Yan najeriya sun fara tofa albarkacin bakinsu dangane da batun kawar da mai baiwa shugaba Goodluck shawara a fannin siyasa, daga kan kujerarsa inda suka bujaci 'yan kasar da suyi addu'ar rokon Allah Ya kawar da duk wani azzalumi a kasar.
Hausawa na cewa komai nisan jifa kasa zai fadi, wannan batu haka yake idan akayi la’akari da abunda ya faru da tsohon mai baiwa shugaban Najeriya shawara akan harkokin siyasa, Ahmed Gulak wanda aka cire daga kujerarsa Talatannan.

Saboda hakan ne, ‘yan Najeriya musamman ‘yan shiyyar arewa maso gabas, sun soma tofa albarkacin bakinsu.

Wani mai suna Gaini Adamu yace “ina yiwa mutanen Najeriya farin ciki da albishir dangane da cire Ahmed Gulak da akayi daga mukaminsa. Duka abinda yayi farko zai ga karshe.”

Sashen Hausa na Muryar Amurka yayi kokarin jin ta bakin Ahmed Gulak, amma bai dauka wayoyin da aka buga mishi ba, sannan bai amsa sakonnin Text da aka aika masa ba.

Mallam Gaini Adamu ya bada shawara ga iyayen daliban Cibok da ‘yan bindiga suka sace, akan suyi zaman dirshen a kofar fadar shugaba Goodluck domin ya fito musu da ‘ya’yansu.

Idan ba’a mance ba, wasu kungiyoyin iyayen yaran sun gudanar da zanga-zanga a birnin Abuja domin gani an fito musu da 'ya'yansu.

Your browser doesn’t support HTML5

Yaya Jama'a Suka Tarbi Korar Gulak? - 3'13"