Zamu Yi Amfani da Na'ura Domin Maganin Cin Hanci Da Rashawa - inji Kwastam

Jirgin ruwa a bakin gabar tekun Najeriya, dake can Ikko.

Shugaban Hukumar Kwastan na Najeriya yace hukumar kwastam ta Najeriya za ta mayar da hankali wajen aiwatar da manufofi biyu domin inganta ayyukanta.
Alhaji Abdullahi Dikko Inde ya fadi haka ne da yake tattaunawa da Aliyu Mustaphan Sokoto cewa horas da ma’aikata da kuma aiki da na’ura mai kwakwalwa su ne suka sa a gaba yanzu domin kawo saukin aiki, da cigaba a hukumar.

Kamar yadda Mr. Dikko ya bayanna, nan gaba mutane baza su yi mu’amala da jami’an kwastom ba ido da ido, sai ta na’u’ra mai kwakwalwa.

Mr. Dikko ya kara da cewa hulda ido da ido kan kawo cin hanci da rashawa, shiyasa suke ganin yin amfani da na’u’ra zai martaba hukumar.

Bisa yadda fasalin ya tsara, ‘yan kasuwa suma zasu shafu daga wannan sauyi, saboda ana bukatar su aika da sako ta na’u'ra zuwa ga hukumar Kwastom, kafi su shigar da kaya Najeriya.