Gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele bai yanke shawarar tsayawa takarar shugaban kasa a watan Fabrairu mai zuwa ko kuma wani mukami da aka zaba ba kuma zai ci gaba da rike mukaminsa na yanzu.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi bulaguro zuwa birnin Abidjan a Cote d'Ivoire domin halartar taron da Majalisar dinkin duniya da ta shirya dangane da kwararowar hamada.
Dakarun rundunar soji ta yammacin Afirka sun kashe mayakan jihadi kimanin 20 a cikin kwanaki uku a wani samame da suka kai a yankin tafkin Chadi, kamar yadda rundunar hadin gwiwa ta sanar a yau Lahadi.
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi kira a jiya Lahadi ga hukumomin soja a Burkina Faso, Guinea da Mali su mika mulki ga farar hula cikin gaggawa, ya kuma tunatar da duniya da ta cika alkawuran “yanayi na gaggawa".
Mataimakin kakakin Majalisar Dinkin Duniya, Farhan Haq ya ce babban sakataren ya isa kasar Senegal da yammacin jiya Asabar, zai kuma tafi Nijar a ranar Litinin da kuma Najeriya ranar Talata sannan kuma ya koma New York.
Buhari ya yi wadannan kalamai a cikin wata sanarwa da kakakinsa, Malam Garba Shehu ya fitar.
Shugaba Buhari ya ce alhakin asarar rayuka da dukiyoyi dole ya hau kan masu daukar matatar man ta haramtacciyar hanya, “kuma dole ne a kama su a kuma a hukunta su.
Wani Ma’aikacin kamfanin Dangote ya ce a wannan watan matatar man za ta fara aiki a kwata na hudu na shekarar 2022.
Akalla mutane 15 ne aka kashe a hare-haren da aka kai a arewa maso gabashin Najeriya cikin makon nan.
Kungiyar IS ta dauki alhakin fashewar wani bam da ta ce ya kashe ko jikkata mutane 30 a wata kasuwa da ake sayar da barasa a jihar Taraba a Najeriya, lamarin da ke nuni da fadada yankin da kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ke kai hare-hare a kasar.
Najeriya dai na fama da matsalar rashin tsaro yayin da wasu gungun 'yan bindiga da ‘yan ta’adda ke kai hare-hare a kan al'ummomi a sassan arewacin kasar.
Wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga, mai suna Nasanda, ya bukaci gwamnatin jihar Zamfara da ta biya shi kudi Naira miliyan 30 saboda kashe matarsa da kawunta da kuma kanwarta ko kuma ya kashe mutum 300 a matsayin ramuwa.
Gwamnatin jihar Legas ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun Chrisland da ke jihar nan take, har sai an kammala gudanar da bincike kan zirgin cin zarafin wata dalibar makarantar a badalance, yayin wata tafiya da suka yi zuwa birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.
Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta kashe mayakan ISWAP fiye da 70 a arewacin kasar da ke kan iyaka da Nijar, a wani samame da ta kai ta sama.
Gwamnatin Biden ta baiwa Najeriya damar siyan manyan jirage masu saukar ungulu na kai hare-hare na kusan dalar Amurka biliyan 1 duk da damuwar da kasar ke da ita ta zargin take hakkin bil adama yayin da kuma take fama da barazanar kungiyoyin 'yan bindiga da masu tsattsauran ra'ayi a arewacin kasar.
Tun shekarar da ta gabata ne Najeriya ta shirya gudanar da kidayar jama’a a amma aka yi watsi da shi saboda karuwar rashin tsaro.
Shugaba Buhari ya umarci hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa (NIWA) da ta kara kaimi wajen tabbatar da tsaron tafiye-tafiyen koguna a kasar.
Gwamnatin Birtaniya ta kulla yarjejeniya da kasar Rwanda domin aikewa da wasu masu neman mafaka zuwa kasar dake gabashin Afirka, matakin da 'yan siyasa masu adawa da 'yan gudun hijira suka yi Allah wadai da shi.
A ranar Litinin ne Mataimakin Shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ya bayyana cewa zai tsaya takarar shugabancin kasar a shekara mai zuwa, lokacin da Shugaba mai ci, Muhammadu Buhari, zai sauka daga mulki.
A ranar Alhamis ne wani alkalin kotun tarayya ya yanke hukuncin cewa, daga yanzu za a ci gaba da gudanar da dukkan shari’ar ta’addanci a Najeriya ta hanyar amfani da fasahar zamani wato ta amfani da bidiyo da kuma ta kafar sadarwa ta intanet.
Domin Kari