Yanzu haka hankulan jama'a sun rarrabu game da maganar kakkabawa Nijar takunkumi da kasashen ECOWAS suka yi akan iyakar Nijar da Najeriya a Birni N'Konni, inda wadansu ke ganin cewa abin zai yi tasiri, yayin da wasu ke cewa, ECOWAS na tauna tsakuwa ne domin baiwa aya tsoro.