Masana tsaro da sauran jama'a a Najeriya na ci gaba da tsokaci tare da nuna jin dadi, a kan labarin mutuwar kasurgumin ‘dan bindigan nan Dogo Gide da aka tabbatar da mutuwar sa a jihar Sokoto.
Tashin hankali tsakanin al'ummomin Hausawa da Fulani a Najeriya na ci gaba da kawo cikas ga kokarin samar da zaman lafiya musamman a yankunan arewacin kasar.
Dan Majalisar Dokoki ta jihar Sakkwato mai wakiltar mazabar Gada ta gabas Honorabul Haruna Dauda ya ce an ceto yaran ne bisa ga kokarin mai baiwa shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu da hadin guiwar gwamnatin jihar Sokoto.
Fatar mutanen Najeriya da Jamhuriyar Nijar ta samun sauki bayan samun nasarar bude iyakokin kasashen biyu na fauskantar cikas saboda kawo yanzu ba a samu wani sauyi na azo a gani ba ni duk da yake Najeriya ta bude iyakokin ta tun makon jiya.
Yayin da al'ummar Musulmi a fadin duniya ke harmar fara azumtar wata mai tsarki na Ramadan, a Najeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, ya ce a fara duban wata daga yau.
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wasu daliban makarantar allo ta almajirao a wani kauye da ake kira Gidan Bakuso a jihar Sokoto da ke Najeriya.
Ana ci gaba da alhinin hadarin jirgin saman mai saukan angulu da ya yi sanadin salwantar rayukan mutane akalla shida ciki har da Shugaban bankin Access, Herbert Wigwe da matarsa da dansa.
Yayin da mahukunta ke kan daukar matakan dakile ayukkan 'yan bindiga a wasu sassa na Najeriya, su kuwa 'yan bindigar na kara kai farmaki ga al'ummomi musamman wadanda ke zaune a wurraren da ke fama da rashin tsaro.
An haifi yaro namiji, a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya, wanda ya zo da gangar jiki daya, da kai biyu, idanu hudu, baki biyu da kuma hanci biyu.
Yayin da al'ummomin wasu yankunan Najeriya ke farin ciki a kan matakan da mahukunta suka dauka wadanda suke fatar su kawo sauki ga matsalar rashin tsaro, wasu kuwa fargaba ce ta karu gun su domin suna ganin barayin zasu kwararo yankuan su ne daga yankunan da aka dauki matakan.
Bayanai sun nuna cewa bayan wadanda 'yan bindigar suka kashe hakama sun yi garkuwa da wasu da ba a san adadin su ba.
Bayanai na nuni da cewa hakan na faruwa ne yayin da matsalar ta rashin tsaro ke raguwa a arewa maso yammcin kasar, kamar a yankunan jihar Sokoto.
Daga daya zuwa gomasha biyar ga Jana'irun kowace shekara, gwamnatin Najeriya, kama da ga matakin tarayya har zuwa jihohi, sukan gudanar da bukukuwa na tunawa da sojojin da suka sadaukar da rayukan su wajen ganin kasar ta tsayu da kafafunta.
Yayin da gwamnatin Najeriya ke cewa tana daukar matakai domin bunkasa ayukkan kasuwanci da habaka tattalin arziki, wasu 'yan kasuwa na kokawa akan cewa har yanzu suna fuskantar kalubale da ke yin tarnaki ga kasuwanci da kuma tattalin arzikinsu.
Wasu sarakuna da suka hada da 'yan majalisar Sarkin musulmi na dakon fuskantar hukunci, sakamakon wani kwamiti da gwamnatin Sakkwato ta kafa don gudanar da bincike akan zarginsu da aikata laifuka masu alaka da siyasa.
'Yan Najeriya na ci gaba da kalubalantar gwamnati akan matakan da take cewa tana dauka da zasu kawo karshen matsalolin tsaro, yayin da ake ci gaba da alhinin kisan kiyashi da aka yi wa jama'a a jihar Plateau.
Yayin da wasu jihohi a Najeriya musamman na arewa ke fuskantar kalubale a bangarori daba daban, hukumomi na duniya na ci gaba da kai dauki domin taimakawa jihohin a sassa daban daban na rayuwa.
'Yan bindiga na ci gaba da cin karensu ba babbaka a wasu yankunan arewacin Najeriya duk da kalaman da mahukunta ke yi na cewa suna daukar matakai na magance matsaloin.
Hukumar yaki da sha ko tu'ammuli da miyagun kwayoyi a Najeriya ta hada hannu da sauran jami'an tsaro domin kara tsaftace al'umma daga illolin tu'ammuli da miyagun kwayoyi, yayin da shekara ta 2023 ke bankwana, bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara ke kara matsowa, .
Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta samar da babura dari bakwai da talatin, domin rabawa jami'ansa kai na banga, domin su rika taimakawa jami'an tsaro na hukuma wajen sintiri don yaki da matsalar rashin tsaro.
Domin Kari