Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ebola Tana Kara Muni A Kasashen Liberiya da Saliyo in ji MSF


Ma'aikatan lafiya a Liberiya dauke da gawar wani mutumi da aka tsinta a kan titi, wanda kuma ake kyautata zaton cutar Ebola ce ta kashe shi.
Ma'aikatan lafiya a Liberiya dauke da gawar wani mutumi da aka tsinta a kan titi, wanda kuma ake kyautata zaton cutar Ebola ce ta kashe shi.

Shugabar kungiyar agajin likitoci ta MSF ta ce annobar cutar Ebola da ake fama da ita, tana matakai dabam-dabam a kasashe uku.

Dr. Joanne Liu ta fada cewa lamarin ya fara daidaita a kasar Guinea, a yayin da cutar ke kara bazuwa gadan-gadan a kasashen Saliyo da Liberiya.

Dr. Liu ta ce ba kamar barkewar annobar wannan cuta ta tsawon kimanin makonni 8 kawai da aka gani a baya ba, a wannan karon zai dauki watanni kafin a shawo kanta. Ta ce wani bambancin kuma a wannan karon shi ne cutar tana shiga manyan garuruwa da birane maimakon a kauyuka kalilan kamar yadda aka gani a baya.

Hukumar kiwon lafiya ta MDD ta ce mutane 1,145 ne suka mutu ya zuwa yanzu daga wannan cuta ta Ebola a Afirka ta Yamma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:00:53 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG