Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mun Yi Nasara Kan Kotun Kasa Da Kasa-Inji OMar al-Bashir Na Sudan


Omar al-Bashir, shugaban kasar Sudan.

Mai gabatar da kara a kotun tace zata karkata akalar binciken zuwa wasu sassa.

Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir yana ikirarin galaba kan kotun kasa da kasa mai hukunuta laifuffukan yaki, bayan da mai gabatar da kara a kotun ya bada sanarwar dakatar da bincike kan laifuffukan yaki da aka aikata a yankin Darfur.

Da yake magana a yau Asabar a khartoum, shugaba Bashir yace al'umar kasar sun sami "galaba"kan kotun kasa da kasar da hkumomin kasar suka ki mika jami'an kasar da ake tuhuma da aikata laifuffukan yaki a yankin Darfur ga kotun da ya kira ta "ta mulkin mallaka".

Yace kotun ta amince cewa ta "gaza" a yunkurin ta na auna bincikenta akansa.

A jiya jumma'a ce dai babbar mai gabatar da kara a gaban kotun Fatou Bensouda tace bata da sauran zabi "illa ta jingine bincike kan shugaba al-Bashir" ta karkata kudaden wajen wasu ayyuka na daban.

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG