Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kenya Ta Zargi MDD da Maida Kwandan Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Sudan ta Kudu Saniyar Ware


Sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD dake Sudan ta Kudu
Sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD dake Sudan ta Kudu

Jakadan Kenya a Majalisan Dinkin Duniya ko MDD ya fada jiya Alhamis cewar babban hafsan sojan Kenya dake jagorancin rundunar kiyaye zaman lafiya a Sudan ta Kudu a lokacin da fada ya barke a kasar a watan Yuli, an maida shi saniyar ware ne a kan gazawar sojojin kiyaye sulhu na MDD wurin kare fararen hula a kasar.

Jakada Macharia Kamau ya shaidawa manema labarai cewar binciken da MDD ta yi don ta binciki lamarin na ranar 8 zuwa 11 ga watan Yuli, an dai yi ne kawai, amma daman an riga an san manufar da ake son a cimma.

Wata hukumar binciken mai zaman kanta da babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya kafa ta dora laifi ne a kan rashin ingantaccen shugabanci a bangaren manyan hafsoshin sojin zaman lafiyar, wanda hakan ne kuma ya yi sanadiyar barkewar fadar da ya janyo har aka kashe mutane kamar 300 a kasar.

A ranar Talata ne MDD ta bada sanarwar cewa a sakamakon bincikenda aka gudanar, ta yanke shawarar gaggauta maye gurbin babban komandan sojojin kiyayen zaman lafiyar , babban hafsin sojan Kenya Lieutenant General Johnson Mogoa Kimani Ondieki

XS
SM
MD
LG