Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mahukuntan Nijar Sun Mika Wa Libya Dan Tsohon Shugaba Gaddafi


Sa'ad Gaddafi a gidan kaso a birni Tripoli bayan da aka mika shi ga hukumar kasar Libya.
Sa'ad Gaddafi a gidan kaso a birni Tripoli bayan da aka mika shi ga hukumar kasar Libya.

An damka dan tsohon shugaban kasar Libya Sa'adi Gadaffi ga mahumkutar kasar Libya a jiya da dare an kuma tasa keyarsa zuwa gidan kaso.

A daren jiya ne mahukumtan kasar Nijer suka damka dan tsohon shugaban kasar Libya Sa'adi Gadaffi hannun mahukumtan kasar Libya dake neman sa ruwa a jallo.

A karshen watan satumba 2011 ne dai wata tawagar kasar Libya ta tsere daga kasar tdomin samu mafaka a kasar Nijer a yayin farmakin da kasashen duniya suka kaiwa kasar Libya domin murkushe niyar Canal Gadaffi,dake neman karewa da fararen hula dake zanga-zangar juyin-juya hali a kasar.

Wanna ya biyo bayan mika Janaral Abdulla Mansur babban jami'in leken asiri na kasar Libya karkashen mulkin Canal Gadaffi da aka yi a watan da ya shige.

Kuma har yanzu kasar Nijer bata ce komai ba dangane da daukan wanna mataki na mika dan na Gadaffi ga kasar.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:05 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG