Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Jahar Adamawa APC na Maida Martani, PDP na Kare Matsayin Ta


Murtala Nyako, gwamnan Jihar Adamawa
Murtala Nyako, gwamnan Jihar Adamawa

APC ta ce bita da kulli, PDP ta ce kyakkyawan manufa, talakawa na cewa da ma an hakura wa'adin mulkin Nyako ya kusa karewa.

Daga cikin 'yan majalisar dokokin jahar Adamawa ishirin da biyar, goma sha tara sun amince da matakin tsige gwamna Murtala Nyako da mataimakin shi Barrister Bala James Ngillari a jiya Laraba. Tuni dai jam’iyar APC da sauran talakawan jahar su ka fara maida martani kan wannan matakin tsige gwamna Nyako da mataimakin shi,

Jam’iyar APC ta maida martanin ne ta bakin kakakin ta Reverend Phineas Padio wanda ya ce yunkurin tsige gwamna Murtala Nyako ba wani abu ba ne illa bita da kulli:
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:53 0:00
Shiga Kai Tsaye

Su ma talakawan jahar Adamawa su na ci gaba da furta albarkacin bakin su akan matakin da majalisar dokokin jahar ta dauka na neman tsige gwamna Murtala Nyako da mataimakin shi Barrister Bala James Ngillari:
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Shiga Kai Tsaye

A na ta bangare, majalisar dokokin jahar Adamawa ta kare matsayin ta da kuma matakin da ta dauka na neman tsige gwamna Murtala Nyako da mataimakin shi. Kakakin majalisar dokokin jahar Adamawa Ahmadu Fintiri ya ce babu wanda ya sa su, sun yi ne da kyakkyawan manufa:
please wait

No media source currently available

0:00 0:01:03 0:00
Shiga Kai Tsaye

An yi ta samun takun saka tsakanin gwamnan jahar Adamawa Murtala Nyako da ‘yan majalisar dokokin jahar tun bayan da gwamnan ya cyi canjin sheka daga jama’iyar PDP mai mulki, ya koma jam’iyar APC ta hamayya.

Haka nan kuma yanayin siyasar jahar yayi zafi ne tun bayan da majalisar ta baiwa kwamishinan ‘yan sandan jahar umarnin kama wasu kwamishinoni hudu ya tsare su saboda sun ki gurfana a gaban majalisar su amsa tambayoyin ta game da yadda ake kashe kudaden gwamnatin jahar. Wakilin Sashen Hausa a jahar Adamawa Ibrahim Abdulaziz ne ya aiko da wannan rahoto.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG