Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Jamhuriyar Nijar Ana Ci Gaba Da Mayarda Martani Akan Korar Tillerson


 Rex Tillerson, sakataren harkokin wajen Amurka da Trump ya kora yana yiwa ma'aikatan ma'aikatarsa ban kwana
Rex Tillerson, sakataren harkokin wajen Amurka da Trump ya kora yana yiwa ma'aikatan ma'aikatarsa ban kwana

Gaf da dawowarsa daga nahiyar Afirka, Shugaban Amurka Donald Trump ya yi waje da Sakataren Harkokin Wajen kasar kana ya nada shugaban CIA ya maye gurbinsa lamarin da ya ba kowa mamaki musamman kasashen Afirkan da Sakatare Rex Tillerson ya kai ziyara

A Jamhuriyar Nijar masana na ci gaba da yin tsokaci dangane da korar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yiwa Sakataren Harkokin Wajen kasar, Rex Tillerson.

Korar tana zuwa ne bayan da sakataren ya kammala ziyarar wasu kasashen Afirka da suka hada da tarayyar Najeriya.

Habib Mummuni sakataren kungiyar malaman makaranta cewa ya yi Donald Trump bai san makamin mulki ba. Ya ce Allah dai ya bashi mulki amma bai san kan mulkin ba. Injishi duk mutanen da suke tare dashi ya koresu daya bayan daya ba tare da yin wani laifi ba. Ya ce ko Amerikawa ma sun fara gajiya da salon mulkinsa.

A nasa ra'ayin magatakardan kungiyar ma'aikata reshen Konni Cuwada Yusuf Adamu yana ganin korar da Donald Trump ya ke yiwa ma'aikatan ba banza ba ne saboda mutanen sun san abubuwan da ya keyi, wato sun san sirinshi dalili ke nan yake korarsu.

Ga rahoton Haruna Mamman Bako da karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:11 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG