Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Jamus Dansanda Ya Harbe Wani da Ake Zaton Dan Gwagwarmayar Islama ne


Shugabar Kasar Jamus Angela Merkel
Shugabar Kasar Jamus Angela Merkel

A kasar Jamus dansanda ya harbe wani dan kasar Iraqi bayan da ya soki wata 'yarsanda da wuka

Wani dan asalin kasar Iraqi wanda ya raunata wata 'yarsanda da wuka ana kyautata zaton dan gwagwarmayar Islama ne kamar yadda aka shaidawa masu gabatar da kara.

Dansanda ya harbe dan Iraqin har lahira bayan da ya yi kokarin kashe 'yarsandar da ya kai ma hari da wuka.

Ranar Alhamis wasu suka kira 'yansanda suka gaya masu wani mutum yana tangatanga tare da kaiwa mutane hari a unguwar Spandau dake birnin Berlin. Daga bisani mutumin ya soki wata jami'ar 'yansanda da wuka kafin wani takwaranta ya harbe mutumin har lahira.

Kafofin labarai sun ce wata kotu dake Stugart ta taba daure mutumin a shekarar 2008 saboda an sameshi da kasancewa dan wata kungiyar ta'adanci.

An bada belin mutumin amma dole ya daura wata naura a kafa wadda zata dinga nuna ma mahukunta inda yake da abun da yake yi a kowane lokaci

XS
SM
MD
LG