Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Abubakar Shekau Ya Sake Bayyana Bayan Ikirarin Kashe shi da Gwamnati tayi


Shugaban ‘yan kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau, Oktocba 2, 2014.
Shugaban ‘yan kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau, Oktocba 2, 2014.

Ana rade-raden cewa ba’a kashe Abubakar Shekau, Shugaban kungiyar Boko Haram ba.

Dangane da rade-raden cewa ba’a kashe Abubakar Shekau, Shugaban ‘yan kungiyar Biko Haram, ba , Shugaban hukumar wayar da kawunan jama’a na gwamnatin Najeriya, Mr. Mike Omeri, yace ba’a bun mamaki bane .

Mr, Omeri, ya furta haka ne a wata hira da yayi da wakiliyar mu Madina Dauda, a birnin Abuja, Omeri ya bada misali da Abukaka, mai watsa labaran, kungiyar bayan da aka kashe shi wani ya fito yace shine saboda haka yace hukumomin Soja sun tabbatar da kashe shi.

A wani jawabi dashi Abubakar Shekau din yayi ya ce yana nan da rai, kuma rashin sa kamar yanda yace ba zai hana gudanar da addini ba.

Ya kuma kara da cewa gwamnati basu da gaskiya, basu da makama basu da abin da zasu fada, yace sai ranar da Allah yayi kwanan sa sun kare kafin ya rasu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:15 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG