WASHINGTON D.C. —
Sabbin alkaluman da hukumar dakile yaduwar cututtuka a Najeriya ta NCDC ta fitar, sun nuna cewa akalla mutum 339 sun sake kamuwa da cutar COVID-19.
Ya zuwa yanzu dai adadin masu cutar gaba daya ya kai 7,016 a fadin kasar.
Har yanzu jihar Legas ce ke kan gaba wajen masu kamuwa da cutar, inda aka samu karin mutum 139.
Bayan nan sai jihohin Kano da Oyo inda suka sami karin mutum 28, 11 a birnin tarayya Abuja, 25 a Edo, 22 a Katsina, 18 a Kaduna, 14 a Jigawa, 13 Yobe, 13 a Filato, 8 a Gombe, 5 a Ogun, 4 a Bauchi, 4 a Nasarawa, 3 a Delta, 2 a Ondo, sai kuma jihohin Adamawa da Rivers da suka samu daya-daya.
Mutum 211 kuma suka rasu sakamakon cutar yayin da mutum 1,907 suka warke.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 25, 2021
Yadda Aka Kama Jabun Magunguna A Jihar Kano Na Sama Da N150M
-
Fabrairu 23, 2021
Ana Samun Nasara A Yaki Da Kanjamau: NACA
-
Fabrairu 22, 2021
COVID-19 :Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kusa Rabin Miliyan A Amurka
-
Fabrairu 10, 2021
Adadin Masu Kamuwa Da Cutar Corona Na Karuwa A Najeriya
-
Fabrairu 03, 2021
Rigakafi AstraZeneca Nada Kaifi Wurin Dakile Yaduwar COVID-19-Oxford
Facebook Forum