Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al-Shabab Ta Kashe Sojojin Tarayyar Afirka Shida


Mayakan Kungiyar al-Shabab
Mayakan Kungiyar al-Shabab

Kungiyar al-Shabab ta kai harin bazata akan sojojin tarayyar Afika inda ta kashe shida ita kuma tayi asarar 11 a ramakon gayya.

Sojojin kungiyar tarayyar Africa su 6 ne aka kashe a hari daban-daban da kungiyar al-shabab ta kai a kudancin Somalia cikin awoyi 24.

KUNGIYAR DAKARUN TABBATAR DA TSARO TA TARAYYAR AFIRKA, wadda ake kira AMISON tace sojojin Burundi 3 ne kungiyar ta al-Shabab ta kashe a ranar Lahadi, lokacin da suka kaiwa tawagan sojojin harin ba zata a wani gari kusa da yakin lardin Shabalele, hakan kuma yayi sanadiyyar wasu sojojin da dama sun samu rauni.

Mai magana da yawun kungiyar ta al-Shabab yace sojoji biyar suka kashe.

Gwamnan jihar Shabalen Abdulkadir Mohammed Nur ya shaidawasashen Somaliya na Muryar Amurka cewa a kalla yan kungiyar na al-Shabab su 11 ne aka kashe sakamakon bude wa juna wuta da akayi dasu da sojojin na Somalia.

Ranar Asabar din data gabata ne kungiyar ta al-Shabab takai wa tawagar sojojin kasar Kenya harin ba zata ta kashe uku daga cikinsu tare da jima sojoji 8 rauni.

Daya daga cikin sojojin kasar Kenya ya shaidawa manema labarai cewa kungiyar ta al-shabab ta kai wa sojojin harin ba zata nea yankin Debio lokacin da suke sintiri. Yace an dauki wadanda suka samu rauni zuwa kasar Kenya cikin jirgin sama.

XS
SM
MD
LG